AdSense

Ganduje ya bada hutun shekarar musulunci a Kano

Gwamnatin jahar Kano ta bada 11/9/2018  hutun sabuwar shekara musulunci wanda yayi dai-dai da  1/1/1440 AH Muharram

Sanarwar ta fito ne daga kwamishinan  yada labarai na jahar Kano Muhammad Garba a yau litinin 10 ga watan na Satumba.

Kamar yadda sanarwar ta nuna, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya taya dukkan al’ummar musulmai murna da farin cikin  shigowa sabuwar shekarar ta  musulunci, ya kuma  kara  da cewa dukkan wani ma’aikacin gwamnati   ya  tsaya tsayin daka da kara kwazo cikin aikin sa dan  samar da cigaba

Gwamna, Ganduje  yayi kira ga dukkan yan Najeriya da su hada hannu da karfe wajan ganin gwamnatin  shugaban kasa Muhammadu Buhari  ta samar da cigaba da zaman lafiya da jituwa a cikin al’umma.



No comments

Powered by Blogger.